Turkiyya na tunawa da waɗanda harin wutar Solingen ya rutsa da su shekaru 32 suka gabata

A shekarar 1993, an kashe ‘yan Turkiyya biyar a garin Solingen na ƙasar Jamus a lokacin da masu kaifin kishin ƙasa suka cinna wa gidansu wuta.
29 May, 2025
Shugaban Turkiyya na ziyara a Azerbaijan don halartar bikin ranar Samun ‘Yancin Kai

Shugaba Erdogan zai halarci taron kasashe uku na Turkiyya-Azerbaijan-Pakistan, da kuma bude Filin Jiragen Sama na Kasa da Kasa na Lachin.
28 May, 2025
Turkiyya ta gudanar da harkokin Hajji da kyau ga mutum 84,000, ta yabi Saudiyya kan ba ta haɗin-kai

Hukumar Harkokin Addini ta Turkiyya (Diyanet) ta ce kasar ta gudanar da ayyukan Aikin Hajji masu girma kuma mafi tsari a bana da ba ta taɓa irinsa ba don taimaka wa mahajjata.
28 May, 2025
Fidan da Putin sun tattauna kan yunkurin sulhu a Ukraine, da kuma batutuwan hulda tsakanin su

Ganawar da Ministan Harkokin Waje na Turkiyya ya yi da Shugaban Rasha ta shafe kimanin sa’a ɗaya, inda aka tattauna kan abubuwan da suka faru a Ukraine bayan taron sulhu na Istanbul.
27 May, 2025

Turkiyya ta yi murnar Ranar Afirka da kuma cika shekara 20 da ƙulla ƙawance da Tarayyar Afirka

An sanya Turkiyya cikin jerin ƙasashen da ka kan gaba wajen yawon buɗe ido da ke kare muhalli

Erdogan ya karbi bakunci Firaministan Pakistan a Istanbul, ya yi alkawarin habaka alaka tsakanin su

Shugaban Turkiyya Erdogan ya tattauna da Shugaban Syria al Sharaa a Istanbul

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu Rasha a ranar Litinin
23 May, 2025
TRT World ta lashe Kambi Hudu a Bikin Kyaututtuka na Fim da Talabijin na ‘2025 New York Festival’
An bayar da kambin ‘Golden Tower’ shirin bin kwakkwafi na TRT World mai suna “Holy Redemption”.

23 May, 2025
Emine Erdogan: ‘Iyali shi ne tushen gina al’umma’
A bikin iyali na ƙasa da ƙasa, Uwargidan Shugaban ƙasar Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira ga duniya ta haɗa kai wajen kare kyawawan ɗabi’u da mutuncin iyali yayin da ake ƙara samun barazana ga ginshiƙan al’adu.

20 May, 2025
Babban jami’in diflomasiyyar Turkiyya ya gana da shugaban kasar Serbia a Belgrade
Shugaban Serbia Aleksandar Vucic ya ce ƙasarsa na mutunta dangantakarta da Turkiyya domin samun kwanciyar hankalin yankin yayin ganawarsa da Hakan Fidan.

19 May, 2025
Shugaban Turkiyya Erdogan ya yi bikin Ranar Ataturk da ta Matsa da Wasanni
‘Muna kare gida da Jamhuriyya kuma muna ɗaukan mataki don bunƙasawa da ɗaga darajar Turkiyya, abin da zai dawwama har abada, a kowane ɓanagre’, a cewar Recep Tayyip Erdogan.

18 May, 2025
Shugaban Turkiyya ya sanar da gano sabuwar rijiyar iskar gas a Tekun Bahar Aswad
Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce sabuwar rijiyar mai ɗauke da cubic meter biliyan 75 na gas, za ta iya wadata gidaje a ƙasar da gas tsawon shekara uku da rabi.

18 May, 2025
Mataimakin ministan harkokin wajen Turkiyya ya kai ziyara Burkina Faso, sun tattauna kan tsaro
Ziyarar da Burhanettin Duran ya kai ta mayar da hankali ne kan daƙile ayyukan ta’addanci da samar da tsaron yanki da kuma ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin Turkiyya da Burkina Faso.

17 May, 2025
Erdogan: Ƙawancen Turkiyya da Amurka wani mabuɗi ne na samun zaman lafiyar yanki da duniya
Shugaba Erdogan ya yi kira da a sake mayar da hankali kan ƙimar haɗin kai da daidaito musamman a cikin tsarin NATO.

16 May, 2025
An fayyace wakilan tattaunawa tsakanin Rasha da Ukraine a Istanbul
Ministan Harkokin Waje na Turkiyya, Hakan Fidan da Sakataren Harkokin Waje na Amurka, Marco Rubio suna ganawa da wakilan Rasha da Ukraine ranar Juma’a.

15 May, 2025
Turkiyya na fatan tattaunawar Istanbul za ta buɗe sabon shafin sulhu tsakanin Ukraine da Rasha
Ministan Harkokin Wajen Hakan Fidan ya bayyana irin rawa mai muhimmanci da Turkiyya ke takawa yayin da ministan harkokin wajen NATO suka yi taro a Antalya a lokacin da ake ƙoƙarin yin sulhu a rikicin Ukraine.

13 May, 2025
Turkiyya na jagoranci a diflomasiyyar kasa da kasa don samar da zaman lafiya – Erdogan
Tuntuɓar baya bayan nan a yaƙin Rasha da Ukraine sun kawo sabbin damarmaki, in ji shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, yana mai ƙara wa da cewa ya yi amanna wannan dama ‘ba za ta lalace ba’.
