Najeriya Tsaro

EFCC ta kama bokaye biyar da jabun kuɗaɗen waje a Osun da Legas

EFCC ta cafke bokaye biyar a Osun da Legas kan zargin damfara da mallakar jabun kuɗaɗen waje da suka kai miliyoyin daloli.

Newstimehub

Newstimehub

18 Dec, 2025

171e9e9271833be6f3b4ef6b26ed61deec1f63662bcf07c26ba90570c6f90924 e1766433922514

Jami’an EFCC na shiyyar Ibadan sun cafke bokaye biyar a jihohin Osun da Legas, bayan bincike ya nuna suna riƙe da jabun kuɗaɗen ƙasashen waje da darajarsu ta kai kusan dala miliyan 3.43 da yuro €280,000, abin da ya sake bayyana yadda ake amfani da sunan tsafi da ruhi wajen yaudarar mutane.

An kama waɗanda ake zargin ne bisa tuhumar damfarar wata mata mai suna Halima Sanni, inda ake zargin sun karɓi naira miliyan 26.55 daga hannunta da sunan za su warware mata matsaloli tare da “tsarkake” ta ta hanyar magungunan ruhaniya.

Waɗanda aka kama sun haɗa da maza biyu da mata uku, kuma an cafke su ne a wuraren ibadarsu bayan wani binciken leƙen asiri da hukumar EFCC ta gudanar a jihohin Osun da Legas.

Bincike ya nuna cewa mutanen suna yaudarar jama’a ne da ikirarin suna da magungunan ruhaniya da kuma aljanu da ke samar da makudan kuɗaɗen waje, inda suke buƙatar wanda aka yaudara ya kawo nasa kuɗin domin aiwatar da abin da suka kira tsarkakewa kafin a “kashe” kuɗin.

EFCC ta ce ban da jabun kuɗaɗen waje, an kwato motoci biyu na alfarma da kuma wayoyin hannu daga hannun waɗanda ake zargin. Hukumar ta tabbatar da cewa za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

Majiyar Labari: Trt Hausa