Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta samu nasarar tsallakawa zuwa wasan dab da na ƙarshe na Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) ta 2025, bayan doke Algeria da ci 2–0 a wasan kwata fainal da aka buga a birnin Marrakech na ƙasar Morocco.
’Yan wasan da koci Eric Chelle ke jagoranta sun nuna bajinta, inda Victor Osimhen ya fara zura ƙwallo a ragar Desert Foxes da bugun kai bayan an dawo daga hutun rabin lokaci, kafin Samuel Akor Adams ya ƙara ta biyu a minti na 57 da bugun ƙwallo mai kyau.
Tun kafin wasan, Super Eagles na cikin kyakkyawan yanayi bayan sun murƙushe Mozambique da ci 4–0 a zagayen ‘yan 16, lamarin da ya kai adadin ƙwallayensu 12 cikin wasanni huɗu — mafi yawa a gasar zuwa yanzu.
Da wannan nasara, Nijeriya za ta fafata da mai masaukin baki, Morocco, a wasan dab da na ƙarshe, yayin da burin ɗaga kofin ke ƙara bayyana ga Super Eagles.














