Kungiyar Independent Hajj Reporters (IHR) ta yi kira ga Hukumar Kula da Ayyukan Hajji ta Ƙasa (NAHCON) da ta gaggauta mayar da kuɗaɗen da suka rage daga kuɗin Hajjin 2025 ga maniyyatan da suka biya fiye da abin da aka kashe a aikace. Kungiyar ta ce jinkirin mayar da kuɗin na iya rage amincewar jama’a da tsarin gudanar da Hajji a Nijeriya.
A cikin wata wasiƙa da ta aika wa Shugaban NAHCON a ranar 19 ga Janairu, wadda shugaban ƙungiyar, Ibrahim Muhammad, ya sanya wa hannu, IHR ta ce bincikenta ya nuna cewa an samu ragowar kuɗi mai yawa sakamakon bambancin farashin canjin kuɗi (exchange rate).
Kungiyar ta bayyana cewa:
An karɓi kuɗin Hajji a kan dala ₦1,600
Amma an biya ayyuka a Saudiyya a kan dala tsakanin ₦1,507 zuwa ₦1,520
Wannan bambanci ya haifar da ragowar kuɗi da ya kai kimanin ₦80,000 zuwa ₦93,000 a kowace dala, inda ake hasashen cewa kowane maniyyaci da ya kammala biyan kuɗi kafin 10 ga Fabrairu na da haƙƙin karɓar kusan ₦437,000 a matsayin ragi.
IHR ta tunatar da cewa NAHCON ta taɓa alƙawarin mayar da ragowar kuɗaɗen bayan kammala lissafin kuɗin bayan Hajji, wanda yanzu aka ce an riga an kammala shi.
Saboda haka, ƙungiyar ta bukaci:
NAHCON ta bayyana jimillar kuɗin da za a mayar cikin kwanaki 7 na aiki
A fara raba kuɗin ga maniyyata ta hannun Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta jihohi cikin kwanaki 14
Kungiyar ta jaddada cewa mayar da kuɗin cikin gaggawa zai rage wa maniyyata wahalar tattalin arziki, tare da ƙara gaskiya da riƙon amana a harkokin Hajji.














