Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya naɗa Pekka Haavisto, tsohon ministan harkokin wajen Finland, a matsayin sabon wakilinsa na musamman kan Sudan. Sanarwar ta ce Haavisto ya maye gurbin Ramtane Lamamra na Aljeriya, inda aka nuna godiya ga ƙoƙarin da ya yi wajen neman zaman lafiya.
Majalisar ta bayyana Haavisto a matsayin gogaggen ɗan siyasa mai kwarewa a harkokin ƙasa da ƙasa. Ya riƙe mukamin ministan harkokin wajen Finland daga 2019 zuwa 2023, kuma a halin yanzu ɗan majalisar dokokin Finland ne. An kuma jaddada ƙwarewarsa a sasanci da tattaunawa, musamman a yankin Horn of Africa da Gabas ta Tsakiya.
Sanarwar ta tuno da rawar da ya taka a baya a cikin tsarin MDD, inda ya taɓa zama Wakilin Musamman na Tarayyar Turai kan Sudan, ya kuma shiga tattaunawar zaman lafiya a Darfur tsakanin 2005 da 2007.
Sudan na fama da rikici mai tsanani tun Afrilun 2023, sakamakon faɗa tsakanin rundunar soji da Rapid Support Forces (RSF). Rahotannin MDD sun nuna cewa rikicin ya haddasa mutuwar dubban mutane, ya raba miliyoyi da muhallansu, tare da haifar da mummunar matsalar jin kai.













