Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana cewa ƙasarsa a shirye take ta fuskanci duk wani hari daga Amurka, yayin da rikici tsakanin Tehran, Washington da Isra’ila ke ƙara tsananta.
A wata hira da tashar NBC News, Araghchi ya ce Iran ba ta tsoron yiwuwar kutsawar sojojin Amurka, yana mai cewa irin wannan mataki zai zama babban bala’i ga Washington.
Kalaman nasa na zuwa ne bayan hare-haren da Amurka da Isra’ila suka fara a ranar 28 ga Fabrairu, hare-haren da hukumomin Iran suka ce sun kashe jagoran addini Ali Khamenei da wasu manyan jami’an tsaro. Duk da ƙara tsanantar rikicin, Araghchi ya ce Iran ba ta nemi tsagaita wuta ba, yana mai jaddada cewa ƙasarsa za ta ci gaba da nuna ƙin amincewa da abin da ta kira matakan da suka saba wa doka da aka ɗauka a kanta.
Ministan ya kuma zargi Amurka da Isra’ila da kai hari kan wata makarantar firamare a Minab da ya ce ya kashe ‘yan mata 171, zargin da Washington ta musanta tare da cewa ana bincike kan lamarin. A cewarsa, Iran ba ta ganin dalilin sake fara tattaunawa da Amurka a yanzu, yana mai cewa hare-haren soji sun lalata duk wani yunkurin diflomasiyya da aka yi a baya.














