China ta fara harba rokoki tare da kaddamar da manyan atisayen soja a zagaye da Taiwan, tana kwaikwayon yiwuwar kulle tsibirin da mamaye shi. Rundunar Eastern Theatre ta ce ana yin atisayen ne da harsashi na gaske, tare da amfani da jiragen yaki, jiragen bama-bamai, jiragen ruwa, da sababbin jiragen saukar ruwa na musamman.
Atisayen, da aka kira “Justice Mission 2025,” sun fara ne kwanaki bayan Amurka ta sanar da tallafin makamai na dala biliyan 11.1 ga Taiwan, kuma su ne mafi girma da Beijing ta taba gudanarwa kan tsibirin. Taiwan ta tabbatar da shiga tarkacen harsashi cikin yankin ruwanta, sai dai ta ce ba ta son tayar da hankali duk da cewa sojojinta sun shiga shirin kare ƙasar.
China ta ce atisayen suna nufin:
Ƙoƙarin kulle Taiwan ta teku da iska
Kwaikwayon kai hari kan manyan tashoshin Taiwan
Gwajin dakile jiragen ruwa, makaman karkashin teku, da kai hari daga sama
Taiwan ta bayyana matakin a matsayin abin da bai dace da babbar ƙasa mai alhakin duniya ba. A yayin da jirage fiye da 130 da jiragen ruwa da dama suka zagaye yankin, kasashen duniya na ci gaba da kallon yadda al’amarin zai kaya, musamman ganin mahimmancin Taiwan Strait ga harkokin kasuwanci na duniya.














