An samu rahotanni cewa an ga Lakurawa na tserewa bayan harin da Amurka ta kai a wasu yankunan Sokoto da Kwara. Harin ya biyo bayan sanarwar da Donald Trump ya yi cewa an kai hari kan ƴan IS a Najeriya.
A Tangaza da Tambuwal (Sokoto), jami’an ƙananan hukumomi sun tabbatar da cewa harin ya sauka a cikin daji da wasu filaye, ba tare da cikakken bayani kan adadin waɗanda suka mutu ba, sai dai an jikkata wasu. Rahotanni sun ce an hango Lakurawa na tserewa daga yankin.

A Offa (Kwara) kuwa, makamin ya faɗa a cikin gari inda ya lalata wasu gine-gine, amma ba a tabbatar da yawan asarar rayuka ba. Gwamnati da mazauna yankin sun tabbatar da faruwar lamarin.
Sojoji sun ce an tura ƙarin jami’an tsaro don hana sake haɗuwar ƴan ta’adda, yayin da Amurka ta nuna yiyuwar ƙarin hare-hare nan gaba.














