Masana na Majalisar Dinkin Duniya sun bayyana fargaba kan makomar wasu maza ‘yan Uyghur 40 da Thailand ta kora zuwa China a watan Fabrairu 2025. Sun ce har yanzu ba a san inda suke ba ko kuma halin da suke ciki, shekara guda bayan mayar da su.
A cikin wata sanarwa, masana sun ce lamarin na nuna abin da suka kira wani salo na danniya da ake yi wa ƙananan kabilu da addinai a wajen iyakokin ƙasa. Sun soki Thailand kan korar mutanen ba tare da kiyaye ka’idar hana mayar da mutum inda zai fuskanci haɗari ba, suna mai gargadin yiwuwar ɓacewa, azabtarwa ko kisa ba bisa ƙa’ida ba.
Masana sun kuma ce mutanen sun shafe fiye da shekara goma a tsare a Bangkok cikin keɓantacce da yanayi mai wuyar sha’ani. Duk da amsar da China ta bayar, sun ce babu sahihan bayanai masu zaman kansu da za su tabbatar da inda mutanen suke.
Sun yi kira ga China ta tabbatar da lafiyarsu tare da bai wa masu sa ido masu zaman kansu damar ziyara. Haka kuma sun bukaci Thailand da sauran ƙasashe su guji korar ‘yan Uyghur zuwa wuraren da za su iya fuskantar haɗari.














