Shugaban Hukumar Raya Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA), Kashifu Inuwa Abdullahi, ya haɗu da masu ƙirƙira da masu tsara manufofi domin lalubo hanyoyin da za su ƙarfafa ci gaban fasaha da ƙirƙira a Najeriya, musamman a yankin Arewa maso Yamma.
A cewar wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X ranar Lahadi, taron ya gudana ne a ƙarƙashin Future Map Foundation Roundtable 1.0 (North-West Edition), inda aka haɗa masu ƙirƙira, ‘yan kasuwa, shugabannin cibiyoyin fasaha da masu tsara manufofi.
Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan ƙarfafa manufofin ƙirƙira na yankuna, bunƙasa haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu, da samar da hanyoyin da za su bai wa sabbin ƙirƙira damar faɗaɗa tasirinsu fiye da al’ummomin da suka fito.
Da yake jawabi a taron, Abdullahi ya jaddada kudirin NITDA na tallafa wa ƙirƙira da ke fitowa daga jama’a, masu dacewa da bukatun cikin gida kuma masu iya gogayya a matakin duniya, bisa tsarin sauya Najeriya zuwa tattalin arzikin dijital. Ya ce haɗin kai mai faɗi na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da cewa ƙirƙira na warware matsalolin al’umma tare da ɗaga darajar Najeriya a kasuwar dijital ta duniya.
Masu halartar taron sun bayyana gogewa da shawarwari kan yadda za a gina cibiyoyin ƙirƙira masu ɗorewa, tallafa wa matasa ‘yan kasuwa, da kuma amfani da manufofi wajen buɗe damar ci gaban yankin Arewa maso Yamma. Taron ya nuna muhimmancin haɗin gwiwa, amincewa da tsari mai ma’ana wajen hanzarta bunƙasar tattalin arzikin dijital na Arewacin Najeriya da ƙasar baki ɗaya.














