A wani ci gaba da ke nuna ingantuwar tsaro a yankin Neja Delta, Rundunar Sojin Nijeriya ta bayyana cewa a duk tsawon shekarar 2025 ba a samu ko da lalata bututun mai guda ɗaya ba a yankin da ke ƙarƙashin kulawar 6 Division, abin da ya nuna nasarar dabarun tsaro da haɗin gwiwar al’umma da hukumomi.
Babban Kwamandan 6 Division, Manjo Janar Emmanuel Emekah, ya ce tun daga lokacin da ya karɓi muƙami a Janairu 2025, ba a samu wata lalata bututun mai ta tashin hankali ba a yankin. Ya danganta nasarar da tsauraran sintiri, bayanan sirri, haɗin gwiwa da jami’an tsaro, da kyakkyawar alaƙa da al’umma.
Ya ce hakan ya taimaka wajen ƙaruwa da yawan man fetur da ake hakowa daga ganga miliyan 1.4–1.5 zuwa kusan ganga miliyan 2.2 a rana zuwa ƙarshen Disamba 2025.
Ya kuma bayyana cewa ba duk zubewar mai ne ke faruwa sakamakon lalata ba, wasu na faruwa ne saboda tsofaffin bututun mai, yayin da sojoji ke ci gaba da yaƙi da satar danyen mai da matatun mai na haramtattu.
A nasa ɓangaren, Daraktan Yaɗa Labaran Tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ya yabawa rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen tallafa wa tsaron ƙasa da gaskiya a aikin sojoji.














