’Yan tseren ƙasar Habasha sun nuna bajinta a gasar Dubai Marathon ta ranar Lahadi, inda Nibret Melak ya lashe tseren maza a karon farko da ya shiga gasar, yayin da Anchinalu Dessie ta dauki zinare a bangaren mata. Habashawa sun kuma mamaye dukkan matakan dandalin mata, suna nuna cikakken rinjayensu a gasar.
Melak ya kammala tseren a cikin sa’o’i biyu da mintuna huɗu, inda ya bar abokin ƙasarsa Yasin Haji da kusan mintuna biyu a baya, yayin da ɗan Rwanda John Hakizimana ya zo na uku. A bangaren mata, Dessie ta rage kusan mintuna huɗu daga mafi kyawun lokacinta, inda ta kammala tseren da sa’o’i biyu, mintuna 18 da sakan 31, bayan da Muliye Dekebo ta fuskanci matsalar ciki a ƙarshen tseren.
Dekebo da Fantu Worku, duk ’yan Habasha ne, sun kammala tseren a matsayi na biyu da na uku, yayin da Dessie ta lashe marathon dinta na uku a jere, bayan nasarori a Seville da Beijing a bara. Ta ce duk da jin daɗin kafa sabon lokaci mafi kyau, tana ganin za ta iya yin abin da ya fi haka a gaba.
A bangaren maza, Melak — wanda ya lashe zinare a tseren mita 10,000 na Gasar Afirka ta 2023 — ya zama ɗan Habasha na shida da ya ci Dubai Marathon a karon farko da ya shiga gasar. Gasar ta bana ita ce karo na 25 na Dubai Marathon, wadda aka sani da shimfidar hanyarta madaidaiciya da ke bai wa sababbin ’yan tseren damar yin fice.














