Hukumar Shigar da Dalibai Manyan Makarantu ta Nijeriya (JAMB) ta sanar da fara sayar da fom ɗin jarrabawar UTME da kuma shigar kai-tsaye (Direct Entry) domin shekarar karatu ta 2026/2027. Hukumar ta ce rajista za ta fara ne daga ranar 26 ga Janairu zuwa 28 ga Fabrairu 2026, yayin da jarrabawar UTME za ta gudana daga 16 zuwa 25 ga Afrilu 2026.
JAMB ta jaddada cewa dukkan masu neman rubuta jarrabawar dole ne su mallaki Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN) kafin rajista. Ta kuma ce dole ne ɗalibi ya kai aƙalla shekaru 16 zuwa ranar 30 ga Satumba 2026, sai dai ‘yan ƙasa da wannan shekaru za su fuskanci tantancewa ta musamman idan sun samu maki sama da kashi 80 cikin 100 a dukkan jarabawar da suka rubuta.
Ga masu neman Direct Entry kuwa, sayar da fom ɗin zai fara daga 2 ga Maris zuwa 25 ga Afrilu 2026 a ofisoshin JAMB na jihohi da shiyyoyi. Haka kuma za a gudanar da Mock-UTME (jarrabawar gwaji) a ranar 28 ga Maris 2026 ga waɗanda suka zaɓa.














