Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Zambia (ACC) ta karrama Detective Sergeant Ruth Nyambe, jami’ar ‘yan sanda a filin jirgin saman Kenneth Kaunda da ke Lusaka, bisa ƙin karɓar cin hanci na dala 50,000. Lamarin ya faru ne a ranar 5 ga Fabrairun 2025, bayan kama wani mutum da ake zargi da mallakar dala miliyan 2.3 da sandunan zinari guda bakwai ba tare da izini ba.
Rahotanni sun ce mutumin ya fara miƙa mata dala 5,000 a matsayin cin hanci, sannan ya ƙara tayin zuwa dala 50,000, amma Nyambe ta ƙi karɓa tare da kai rahoton lamarin ga Hukumar Yaki da Miyagun Kwayoyi (DEC), abin da ya taimaka wajen ci gaba da bincike da kamun wanda ake zargi.
Saboda gaskiyarta, ACC ta ba ta Kyautar Gaskiya, yayin da Babban Sufeton ‘Yan Sanda na Zambia ya ɗaga mata matsayi daga Sergeant zuwa Inspector. Haka kuma, an yabawa wasu jami’an gwamnati da ‘yan sanda a ƙasar bisa ƙin karɓar cin hanci, a matsayin wani ɓangare na yaƙi da rashawa a Zambia.














