Afirka

‘Yar sanda ta samu karramawa bayan ƙin karɓar cin hancin dala 50,000 a Zambiya

ACC ta karrama ‘yar sanda Ruth Nyambe a Zambiya bayan ta ƙi karɓar cin hancin dala 50,000 daga wanda ake zargi da fasa-ƙwaurin kuɗi da zinari a filin jirgin Lusaka.

Newstimehub

Newstimehub

26 Dec, 2025

80b634362379c8dcaaf790d366666e8c804f0362a6dba90353e9e93c3356ab45 main e1766766757367

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Zambia (ACC) ta karrama Detective Sergeant Ruth Nyambe, jami’ar ‘yan sanda a filin jirgin saman Kenneth Kaunda da ke Lusaka, bisa ƙin karɓar cin hanci na dala 50,000. Lamarin ya faru ne a ranar 5 ga Fabrairun 2025, bayan kama wani mutum da ake zargi da mallakar dala miliyan 2.3 da sandunan zinari guda bakwai ba tare da izini ba.

Rahotanni sun ce mutumin ya fara miƙa mata dala 5,000 a matsayin cin hanci, sannan ya ƙara tayin zuwa dala 50,000, amma Nyambe ta ƙi karɓa tare da kai rahoton lamarin ga Hukumar Yaki da Miyagun Kwayoyi (DEC), abin da ya taimaka wajen ci gaba da bincike da kamun wanda ake zargi.

Saboda gaskiyarta, ACC ta ba ta Kyautar Gaskiya, yayin da Babban Sufeton ‘Yan Sanda na Zambia ya ɗaga mata matsayi daga Sergeant zuwa Inspector. Haka kuma, an yabawa wasu jami’an gwamnati da ‘yan sanda a ƙasar bisa ƙin karɓar cin hanci, a matsayin wani ɓangare na yaƙi da rashawa a Zambia.

Majiyar Labari: Trt Hausa