Najeriya Siyasa

Ganduje Ya Janye Shirin Kafa Rundunar Hisba Fisabilillah a Kano

Tsohon gwamnar ya janye ƙudirin kafa rundunar Hisba Fisabilillah a Kano bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki, sakamakon martanin jama’a da damuwar da lamarin ya haifar.

Newstimehub

Newstimehub

16 Dec, 2025

03a0bb46 edfe 4d06 94a6 08840089db08.jpg e1765913778184

Tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya sanar da janye ƙudirinsa na kafa rundunar Hisba Fisabilillah. Wannan mataki ya biyo bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki daga ƙananan hukumomi 44 na jihar, wanda ya haifar da shawarar dakatar da shirin. Sanarwar ta bayyana cewa an yanke wannan hukunci sakamakon martanin jama’a da damuwar da lamarin ya haifar, inda aka cimma matsaya na warware matsalar ta hanyar tattaunawa.