Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC ta isa gidan El-Rufai da misalin karfe 2 na rana, inda suka fara bincike a duk faɗin gidan. Hakan ya tabbata ne a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin watsa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar.
Lauyan El-Rufai, Ubong Akpan, ya soki samamen, inda ya bayyana shi a matsayin “ba bisa doka ba kuma ya keta hakkokin bil-adama da ka’idojin shari’a.”
ICPC ta tabbatar ranar Laraba, 18 Fabrairu 2026, cewa El-Rufai na hannun ta a yayin da ake ci gaba da bincike. Wannan na zuwa ne bayan jerin zarge-zarge da kuma hulɗa da hukumomin tsaro.
Kwanaki uku kafin haka, El-Rufai ya ziyarci hedkwatar EFCC a Abuja kan zargin almundahana yayin mulkinsa daga 2015 zuwa 2023. Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaro sun yi yunƙurin kama shi bayan dawowarsa daga Cairo, Misira.
Bugu da ƙari, DSS ta shigar da kara mai tanadi guda uku kan zargin El-Rufai da satar bayanai daga wayar Nuhu Ribadu, wanda ake ganin ya saba sashe na 12(1) na dokar Cybercrimes (Prohibition, Prevention, etc.) (Amendment) Act, 2024.
Majiyar Labari: Channels News














