Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi gargaɗi ga gwamnonin jihohi cewa zai iya fitar da umarnin shugaban ƙasa domin tilasta biyan kuɗaɗen kananan hukumomi kai tsaye, idan ba su aiwatar da hukuncin Kotun Koli kan ’yancin kuɗaɗen ƙananan hukumomi ba. Tinubu ya yi wannan gargadi ne a taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC da aka gudanar a Abuja.
Ya jaddada cewa Kotun Koli ta riga ta bayar da umarni na biyan kuɗaɗe kai tsaye daga asusun tarayya zuwa kananan hukumomi, inda ya nuna cewa jihohi ba su da ikon riƙe ko sarrafa kuɗaɗen da suka dace da ƙananan hukumomi. Tinubu ya buƙaci gwamnonin su mutunta hukuncin kotu, yana mai gargadin cewa zai ɗauki mataki idan aka ci gaba da ƙin aiwatarwa.
Shugaban ƙasar ya kuma yabawa jam’iyyar APC bisa nasarorin da ta samu, tare da kira ga jam’iyyar ta ƙarfafa tsari a matakin kananan hukumomi. Bugu da ƙari, ya goyi bayan kafa ’yan sandan jihohi, ya jaddada yaƙi da ’yan ta’adda da ’yan bindiga, ya nuna goyon baya ga shigar mata cikin kundin tsarin mulki, sannan ya yi watsi da tsoma bakin gwamnatin tarayya kan batun caca.














